Kalli Abinda Tura Yan Mata Talla Ya Jawo Anyiwa…

Mun samu wani rahoto wanda babu wata kwakkwariyar hujja kan shi amma abu ne wanda yake faruwa yau da kullum a wannan zamani ko muce musifa ce wacce take damun mutanen wannan lokaci.

Yarinya yar shekara biyar saika samu labari wani yayi mata fyade karshe ma ka samu labarin ta rasa ranta sanadiyar wannan mummunan aiki da akayi da ita. Mun samu wannan rahoto ne a YouTube channel.

An samu nasarar tono asirin wasu mutane wanda ake zargin su da lalata rayuwar kananan yara mata da yara yan talla wannan ba sabon abu bane, sannan laifin yana a kan iyayen yaran domin duk yarinyar da zatayi talla sai da iyayen su amince.

Sannan duk wata yarinya da zata fito gida sakacin iyaye ne domin koda kuwa basu san lokacin da su fita ba. Dalili iyaye kiwo ne Allah ya basu na yara dole su kula dasu kamar yadda suke kula da dukiyoyinsu fiye da yadda suke kula da dukiya.

Misali idan yau da tunkiya ce ko akuya. Suka san idan ta fita za’a sace ta zaku ga kullum hankakinsu yana kan wannan tunkiya ko akuya domin kada ta fita basu sani ba. Irin wannan kulawar itace kwatankwacin wacce ake so ku nunawa yaran da Allah ya baku kiwo. Inji daya daga cikin wanda suyi nasara tono asirin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
X
DANNA NAN KAGA BIDIYAN πŸ‘ˆπŸ˜­πŸ’£πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡¬